| تعداد آیه | حزب | جزء | صفحهی شروع | محل سوره |
|---|---|---|---|---|
| 8 | 120 | 30 | 599 | مدینه |
Idan aka girgiza ƙasa, girgizawarta. ١ Kuma ƙasa ta fitar da kayanta, masu nauyi. ٢ Kuma mutum ya ce "Mẽ neya same ta?" ٣ A rãnar nan, zã ta faɗi lãbãrinta. ٤ cewa Ubangijinka Ya yi umurni zuwa gare ta. ٥ A rãnar nan mutane za su fito dabam-dabam domin a nuna musu ayyukansu. ٦ To, wanda ya aikata (wani aiki) gwargwadon nauyin zarra, na alheri, zai gan shi. ٧ Kuma wanda ya aikata gwargwadon nauyin zarra na sharri, zai gan shi. ٨